Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    A Ƙarshe Gwamnatin Buhari Zata Soke Kungiyar ASUU

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 23, 2022Updated:August 23, 20221 Comment2 Mins Read

    Kamar yadda binciken mu ya gano alamu sun bayyana a jiya cewa gwamnatin tarayya na iya duba yiwuwar haramta kungiyar malaman jami’o’i, ASUU idan har ta kasa janye yajin aikin da ta dade bayan tayi mata tayin dakatar da shi.

    Gwamnatin tarayya ta kuma amince da karin Naira biliyan 100 ga bangaren jami’o’in a wani bangare na fahimtar juna da sake tattaunawa kan yarjejeniyar 2009.

    Baya ga haka, an amince da Naira biliyan 50 daidai da yadda kungiyoyin da ke jami’o’i za su raba a matsayin alawus-alawus.

    Kungiyoyin hudu na jami’o’i da ke takun-saka kan biyan kudaden alawus-alawus din su ne ASUU, wacce ta kira nata kudaden da ake ba su albashi, da manyan ma’aikatan jami’o’in Najeriya, SSANU, kungiyar ma’aikatan da ba malamai ba ta, NASU da Ƙungiyar Ƙwararrun, NAAT.

    Zan Mayar Da Jami’o’i Karkashin Kulawar Gwamnatocin Jihohi Idan Na Zama Shuagaban Kasa – Atiku

    Dan takarar shugaban kasa a bababr jam’iyyar PDP, Atiki Abubakar, ya lashi takobin mika wa gwamnatocin jihohin ragamar kulawa da Jami’o’in gwamantin tarayyar, idan ya lashe zaben 2023.

    Atiku, ya bayyana haka ne yayin wani babban taro na kungiyar lauyoyin Najeriya da ya gudana a Jihar Legas.

    An ruwaito Atiku ya ce kadarorin da Najeriya ta mallaka na iya karewa nan ba da dadewa ba.

    “Daya daga cikin abubuwan da na shirya yi shi ne karfafa wa bangaren ‘yan kasuwa na cikin gida da na waje da su zuba jari a banagren ilimi domin Najeriya ba ta da kadarorin da za su dade tana sarrafa su kamar yadda take yi a yanzu.”

    Ya kuma yi tsokaci kan talaucin da ya addabi yawancin ‘yan kasar, inda ya ce “tun bayan da Najeriya ta koma bisa turbar dimokradiyya a 1998 zuwa 1999, kasar ba ta taba samun kanta cikin tasko kamar wanda ta ke ciki ba a yanzu.”

    Atiku ya yi alkawura da dama kan sauya wasu fasali na kadarorin Najeriya ciki har da sayar da Babban Kamfanin Mai na Kasa (NNPC).

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Ahmed usman yero on August 23, 2022 9:39 pm

      [email protected]

      Reply
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.