AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » A ƙarshe Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kawo ƙarshen Yajin Aikin ASUU
    News

    A ƙarshe Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kawo ƙarshen Yajin Aikin ASUU

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiJuly 10, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Karamin ministan ilimi, Goodluck Opiah, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari na kokarin kawo karshen yajin aikin malaman jami’a (ASUU) nan bada jimawa ba.

    Ministan ya bayar da tabbacin ne a Owerri, babban

    birnin jihar Imo a karshen mako yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a yayin wani liyafa da abokansa suka shirya masa.

    Ya ce:

    “Zan iya tabbatar maku cewa gwamnati ta damu sosai game da lamarin. Har yanzu da nake magana da ku tunane-tunane da dama, tattaunawa da dama da taruka na gudana da nufin magance lamarin cikin gaggawa.”

    Ya bayyana fatansa cewa za a kawo karshen rashin jituwa nan ba da jimawa ba, jaridar The Nation ta rahoto.

    Ya kara da cewa:

    “Ina kyautata zaton cewa za a magance rashin jituwar da ke tsakanin gwamnati da malaman ASUU nan ba da jimawa ba domin yaranmu su koma makaranta.”

    Ministan ya ce matsalolin da ke ma’aikatar ilimi na da wuyar gaske kuma gwamnatin tarayya bata yi kasa a gwiwa ba wajen neman mafita da kawo karshen yajin aikin kungiyar ASUU.

    Ya ce a shirye yake ya bayar da gagarumin gudunmawa a ma’aikatar ta hanyar aiki tare da ministan ilimi, Mallam Adamu Adamu, rahoton The Cable.

    Ya ce:

    “A shirye nake na bayar da gudunmawa a ma’aikatar da bangaren ilimi ta hanyar aiki tare da ministan, Mallam Adamu Adamu. A duk inda matsaloli suke dole akwai mafita. Kuma ina iya tabbatar maku cewa za mu nemo mafita kuma yaranmu za su koma makaranta.”

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.