AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Abin Mamaki Baya Karewa! Wani Matashi Ya Auri Kanwarsa
    News

    Abin Mamaki Baya Karewa! Wani Matashi Ya Auri Kanwarsa

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 4, 20221 Comment2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Munyi karo da wani labari na wata mata ta yi matukar mamaki a ranar auren danta, yayin da ta gano cewa ashe amaryar ’yarta ce wacce ta bace tun shekara 20 baya.

    Hakan ya sa mahaifiyar amaryar wacce a rashin sani ta kusa ta zamar mata surika suka fara zubar da hawaye, ita da amaryar da angon, tun bayan da suka gano cewa ita ce ’yarta wacce ta bace da dadewa kuma yanzu take auren danta.

    An dai gudanar da wannan bikin ne a garin Suzhou, da ke lardin Jiangsu na kasar China a ranar 31 ga watan Maris.

    Sabuwar surikar ta gano ’yar tata ce a lokacin da ake cikin tsakiyar biki, inda ta tabbatar da ’yarta ce ta hanyar gano irin hannunta, kamar yadda kafar yada labarai ta Times Now News ta ruwaito.

    Ita dai wannan matar ta fuskanci wadanda suke ikirarin su ne iyayen amaryar, sannan ta tambaye su ko su ne masu rainon amaryar, sai ’yan uwan amaryar suka yi mamakin tambayar da mahaifiyar ke yi masu, duk da yake labari ne mai tsawo.

    Daga nan sai suka fara bayyana abin da ya faru da amaryar tun tana jaririya kamar haka: “Wadanda suka raini amaryar sun ce, sun tsinci jaririya a gefan hanya, sai suka dauke ta suna rainonta har ta girma. Kuma sun raine ta kamar ’yar da suka haifa.”

    Ita dai wannan batacciyar yarinya ta bayyana yadda ta yi murnar haduwarta da mahaifiyarta fiye da murnar ranar bikinta.

    Bayan ta gano abin da ya faru, sai ta nuna damuwarta game da auren, duk da yake shi ma angon dan riqo ne, inda ta karkata ga dan uwan nata.

    Angon ya bayyana aniyarsa na auren matarsa kuma ya ce, ba wani dalili na sauya kudirinsa.

    A bangaren mahaifiyar, ta ce ba wata matsala a auren tun da ba ’yan uwa ba ne na jini domin kuwa shi ma angon dan riko ne da aka dauko tun yana karami.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Bilya hussain on September 5, 2022 6:09 am

      Allah yakyauta

      Reply

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.