AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Akwai Babbar Matsala: Rikicin Ali Nuhu Da Hannatu Bashi Ya Dauki Sabon Salo
    Kannywood

    Akwai Babbar Matsala: Rikicin Ali Nuhu Da Hannatu Bashi Ya Dauki Sabon Salo

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiOctober 25, 2022No Comments4 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Kotun Majistare ta 54 da ke Nomanslan a birnin Kano a karkashin jagorancin Mai shari’a Aminu Gabari ta nemi jarumar finafinan Hausa da aka fi sani da Kannywood, Hannatu Bashir ta bayyana a gabanta a zama na gaba ba tare da ta turo lauyanta don wakiltarta ba.

    Tun farko jarumi Ali Nuhu ne ya yi karar jarumar bisa zargin cin mutuncinsa ta waya sakamakon rashin halartar daukar wani fim dinta da ya yi.

    Tun a baya da take zantawa da manema labarai, Hannatu Bashir ta ce ta gayyaci Ali Nuhu don fitowa a wani fim din da ta shirya inda suka yi yarjejeniyar za a dauki fim din a ranar 10 ga Oktoba.

    Sai dai Ali Nuhu bai halarci wurin daukar fim din ba lamarin da ya fusata jaruma Hannatu ta aika masa da sakon tes wanda shi ma ya aike mata da amsa.

    “Abin da ya bata min rai a wannan magana shi ne da kansa Alin ya zabi wannan ranar da muka yi za a dauki fim din, amma bai zo ba kamar yadda ya yi alkawari haka kuma bai bayar da wani uzuri na yin hakan ba.

    Sai na aika masa da sakon tes wanda a fahimtata ban yi amfani da kalmomi masu zafi ba. Shi ma ya aika min da amsa wanda ya yi min zafafan kalamai, amma ganin cewa shi babba ne sai na hakura ban sake aika masa da wata mummunar magana ba.”

    A cewar Hannatu ita ya dace ta yi karar Ali Nuhu ba shi ya yi kararta ba.

    A cewar Hannatu duk da cewa ba su yi yarjejeniya a rubuce ba amma shi kansa Ali Nuhu ba zai musanta hakan ba.

    Aminiya ta ga wasu daga cikin sakonnin, inda a ciki Ali Nuhu yake cewa ba wai sun yi wata yarjejeniya ba ce a rubuce, don haka bai kamata ta turo masa sakonnin da ta tura masa da maganganun da cewarsa zafafa ne ba.

    A hoton da ake zargi na sakon ne da Aminiya ta gani, an ga Hannatu na cewa Ali Nuhu bai yi mata adalci ba domin a cewartsa tun watan jiya ta so ta yi aikinta, amma daraktan shirin, wanda shi kuma na hannun damar Ali Nuhu ne, Sheikh Isa Alolo ya ce mata Alin yana aiki, a bari sai ya gama.

    Ta kuma fada a cikin sakon cewa Alolo ya fada mata cewa Ali Nuhu ya ce 10 ga wata (Oktoba) za a yi, sannan ana gobe za a fara aikin ta ce ta kara magana, domin a cewarta idan ba a fara aikin ba a ranar akwai matsala.

    A karshe ta ce, “Ba matsala na hakura, kuma insha Allah fim ko kyauta za ka yi min, ba zan sake sa ka ba in Allah Ya yarda.”

    A wani martani da ake yadawa cewa Ali Nuhu ya mayar, wani hoton da Aminiya ta gani yana cewa ne, “Me na yi miki da za ki turo min irin wannan sakon?

    Ali Nuhu ya kara da cewa zai dauki matakin hukuma, inda a cewarsa za ta yi bayanin kudin da ta biya shi, ko yarjejeniya da suka yi da ya saba.

    A game da hakan, jaruma Hannatu Bashir ta ce lallai ba su yi rubutu ba, amma a cewarta, “Gaskiya kamar yadda muka saba mun yi magana ne kawai a waya babu wani rubutu da muka yi.

    Kasancewar muna ganin mun zama daya ba mu yin abubuwanmu a rubuce.

    Amma duk da haka shi kansa Ali ba zai musanta wannan yarjejeniya da muka yi ba.”

    Sai dai a ranar Talata Hannatu ba ta samu damar halartar zaman kotun ba, sai dai lauyanta hakan ya sa Alkalin Kotun Mai shari’a Aminu Gabari ya nemi ta bayyana gaban kotun inda kuma ya dage zaman shari’ar zuwa ranar 25 ga Oktoba, 2022.

    Aminiya ta leka shafin Instagram na Hannatu Bashir, inda ta gano cewa jarumar tana can Jihar Gombe, inda ake daukar wakar Dauda Kahutu Rarara ta Jagaba Shi ne Gaba.

    Sai dai a wani lamari mai cike da ban-mamaki, an gano hoton jarumar tare da Forudusa Abubakar Bashir Maishadda suna zaune, inda a kasan hoton ya rubuta cewa, “Cif El-Mu’az ga ni ga mutuniyar muna jiranka a Gombe.”

    Hannatu Bashir dai mutuniyar El-Mu’az Birniwa ne, sai dai shi kuma Maishadda babban na hannun damar Ali Nuhu ne, wanda ya ba wasu mamaki ganin ya sa hoton jarumar tare da shi suna murmushi a daidai lokacin da take kotu da Ali Nuhu.

    An dai dade ba a ga Maishadda da Ali Nuhu ba, musamman a wajen wakokin Rarara da a da can Ali Nuhu yake bayar da umarni.

    Shin ko dai su ma sun samu sabani ne sun raba gari? Wannan dai lokaci ne zai bayyana.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Shin Dagaske Ne Jaruma Fati Washa Tafi Duk Matan Kannywood Kyau?

    November 24, 2022

    Jaruman Kannywood Sun Jawowa Kansu Magana Saboda Wannan Bidiyo Da Sukayi

    November 20, 2022

    Kalli Bidiyon Maryam Yahaya Tana Rawar Yan Kauye Kafin Ta Shiga Harkar Fim

    November 18, 2022

    Junaidiyya Gidan Badamasi Ta Bayyana Dalilin Dayasa Ta Fito Daga Gidan Mijinta Ta Fara Harkar Fim

    November 18, 2022

    Jerin Matan Da Adam A Zango Yayi Soyayya Dasu A Kannywood

    November 18, 2022

    Kalli Abinda Hamisu Breaker Da Momee Gombe Sukayi A Gidan Gala Wanda Ya Jawo Musu Magana

    November 16, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.