AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » An Kamashi Ya Yiwa Budurwa Fyade A Makabarta
    News

    An Kamashi Ya Yiwa Budurwa Fyade A Makabarta

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 9, 2022No Comments3 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Labarin da muke samu a yau shine rundunar ‘yan sandan jihar Gombe sun gabatar da kama wani mutum da ake zargi da yi wa wata yarinya mai shekara 16 fyade a makabarta a karamar hukumar Kaltungo da ke jihar Gombe.

    Kamar yadda majiyar amihad.com ta tabbar batun hakan na dauke ne a wata takarda mai dauke da sanya hannun Kakakin rundunar, ASP Mahid Mu’azu Abubakar a madadin Kwamishinan ‘yan sandan jihar ne Ishola Babatunde Babaita.

    Ya ce magidancin mai suna Reuben Azariah na makwabtaka ne da yarinyar da ake zargin ya yi wa fyaden.

    ASP Mahid, ya ce jami’an ‘yan sanda a karamar hukumar Kaltungo sun samu rahoton hakan ta wajen wata mai suna Abigail Yunusa, mahaifiyar yarinyar da aka yi wa fyaden.

    Majiyarmu jaridar Aminiya ta rawaito cewan ASP Mahid ya ce a ranar biyu ga watan Satumbar 2022 da misalin karfe 8:30 na dare ne ita Abigail Yunusa da ke zaune a unguwar Tarmana a karamar hukumar ta Kaltungo ta kai musu rahoton shi wanda ake zargin Reuben Azariah da suke zaune da shi a unguwa daya kan cewa ya yiwa ‘Yar ta da aka (sakaye sunanta) mai kimanin shekara 16 fyade da karfin tsiya a kan wani kabari da ke harabar gidan da suke a nan unguwar Tarmana.

    A cewarsa, daga karbar rahoton ‘yan sanda suka shiga neman sa inda suka yi nasarar kamo shi Reuben, aka kuma dauke shi da yarinyar duka aka kai su babban asibitin garin kaltungo domin a duba lafiyarsu.

    Daga nan ya ce da zarar sun kammala bincikensu na ‘yan sanda za su tura shi wanda ake zargin zuwa kotu.

    Har ila yau a wani labari mai kama da wannan Jami’in hulda da jama’ar yace yan sanda sun kama wani mai shekaru 55 a Gombe mai suna Musa Umar da shi ma ya yiwa yar shekara 6 fyade a wani kango da ba’a kammala ba a unguwar Kagarawal.

    ASP Mahid Mu’azu ya ce ‘yan sanda sun samu korafi ne daga wani mazaunin unguwar Alhaji Musa Shehu, na shi Musa Umar mai shekara 55 da ke zaune a unguwar ta Kagarawal, inda ya yaudari wata yarinya mai shekara shida ya dauke ta zuwa wani kango ya yi mata fyade.

    Daga nan ya ce suna karbar korafin suka tsunduma nemansa suka kuma kamo shi, da shi da yarinyar sun kai su asibiti dan duba lafiyarta, shi kuma daga bisani za su tura shi zuwa kotu.

    Related

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.