• Fri. Mar 29th, 2024

Amihad.com

Number 1 Financial Education and Tech Blog

An Sace Wayar Bature A Ingila Ya Ganota A Nijeriya Cikin Yan Kwanaki

ByLucky Murakami

Oct 15, 2022

Wani bature dan Ingila ya bayyana yadda ya gano wayarsa a Najeriya bayan wata guda kacal da ta yi batar dabo.

Baturen mai suna, Darren, ya bayyana afkuwar wannan lamari ne a shafinsa a Twitter.

Cikin mamaki mutumin ya wallafa a shafinsa na Twitter bayan wata daya da batan wayarsa a birnin Liverpool amma kuma da ya yi bincike ta manhajar iCloud sai ya gano cewa a halin yanzu wayar tana Jihar Edo a Najeriya.

Ya dai sanya bayanan da ya samo kai tsaye a shafinsa na Twitter domin ya shaida wa mutane inda wayar tasa take a wannan lokaci.

“Na rasa wayata wata daya ke nan yanzu a garin nan…, yanzu ina shiga iCloud dina sai nake ganin cewa wayar tawa ta tafi hutu Najeriya,” a cewar Darren.

By Lucky Murakami

A savant on system network security and information technology with adept leadership skills.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *