AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Asirin Shugaban Makaranta Da Yayi Lalata Da Dalibai Mata 7 Ya Tonu
    News

    Asirin Shugaban Makaranta Da Yayi Lalata Da Dalibai Mata 7 Ya Tonu

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 10, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Rahoton da muke samu shine dambarwa ta biyo bayan zargin lalata da dalibai bakwai da ake yi wa Shugaban Kwalejin Musulunci ta Hassanat da ke Ilori a Jihar Kwara.

    Kamar yadda binciken mu ya tabbatar wasu kafafen yada labarai sun rawaito cewa shugaban mai suna Samuel Prosper ya buya, tare da rokon a yafe masa.

    To sai dai binciken majiyarmu jaridar Aminiya tayi ya nuna a ranar Alhamis gwamnati ta rufe makarantar, sai dai zanga-zangar shugabbaninta ya sanya Ma’aikatar Ilimi sake bude ta.

    Wata ma’aikaciuya da ta nemi a sakaya sunanta ta ce duk da shugaban da ake zargi ya ajiye aiki, makaranatar ba ta da dalibai masu sunyaen da kafafen yada labarai suka rawaito a makaranatar.

    Ta kuma ce sunaye biyu ne kadai na dalban nasu, suma kuma sun karyata labarin.

    Ta ce kafin wannan lokacin, shugaban makaranatar ya sha korafin ana yi wa rayuwarsa barazana, musamman kasancewarsa Kirista da ke jagorantar makaranatar Musulmi mai zaman kanta.

    “Shi kuma shugaban riko ne, kasancewar tsohuwar shugabar ta samu wani aikin a Abuja.

    “Da yake shi ne mataimakinta, sai aka ba shi kafin zabar wani sabon shugaban kuma ana tsaka da haka ne mai makarantar ya rasu,” in ji ta.

    Wata makwabciyar makarantar, Misis Mojirayo, ta ce, “Ba mu taba jin wannan labarin ba sai yau da safe.”

    Har ila yau, kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kwara, Ajayi Okasanmi, ya ce babu wani dan jarida da ya tabbatar wa faruwar lamarin.

    “Abin da na ce shi ne babu wanda ya shigar da korafi makamncin wannan ofishinmu,” in ji shi.

    A nasa bangaren, kakain ma’aikatar ilimi ta jihar, Peter Amongbonjaye, ya ce ba shi da hurumin yin magana kan lamarin.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.