AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Bayan Bankin Duniya Ya Dauki Nauyin Karatunta Yan Jarida Sunyi Hira Ta Yarinya Mai Baiwar Lissafi
    News

    Bayan Bankin Duniya Ya Dauki Nauyin Karatunta Yan Jarida Sunyi Hira Ta Yarinya Mai Baiwar Lissafi

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 7, 2022Updated:August 7, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Wani labari daya shigo mana ya tabbatar mana da cewa Saratu Dan-Azumi, wata ‘yar matashiya daga jiharKano ta sake samun daman gurbin karatu saboda kwakwalwan da Allah ya bata na kwarewa a fannin Lissafi.

    Kwanan nan aka gano cewa yarinyar ashe ba ta zuwa makaranta amma duk da haka tana iya lissafin lambobi kamar mai aiki da kwanfuta,wanda har ta yi nssarar samun talafin karatu daga gidauniyar Bashir Ahmad, BAF.

    Mutane da dama sun yi ta tsokaci tare da bayyana jin dadinsu game da irin baiwar da Allah Ya yi wa Saratu, ’yar asalin kauyen Gwadayi, Gundumar Shagogo a Karamar Hukumar Gaya ta Jihar Kano.

    Bidiyon Hira Da Yarinya Mai Baiwar Lissafi Da Ta Samu Tallafin Karatu Har Zuwa Jami’a

    https://www.youtube.com/watch?v=clyuCUsKdz8

    Tallafin Da Saratu Ta Samu

    Saratu ta samu tallafin ne a karkashin shirin tallafawa mata don su yi ilimi (AGILE), wanda Bankin ke daukar nauyi a jihar Kano.

    Amihad.com ta samo wannan labari ta hanun Malam Aliyu Musa, Jami’i Yada Labarai na shirin wanda shine ya bayyana haka ga Kamfanin Dillacin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Laraba.

    Malam Yusuf wanda kuma shi ne Mataimakin Daraktan yada labarai na Ma’aikatar Ilimi ta jihar Kano ya ce, ofishin kula da shirin na Bankin Duniya a jihar Kano ya bayar da umarni a zakulo yarinyar nan a kuma sa ta a makaranta.

    “Sai a ka yi sa a, masu kula da shirin ilimin mata na AGILE na tsaka da ziyara zuwa masarautu biyar na jihar Kano don neman hadin kan sarakuna kan batun ilimin mata a jihar,” inji shi.

    A yayin ziyararsu a masarautar Gaya ne jami’an suka yi wa Sarki bayanin yarinyar da kuma aniyarsu ta daukar nauyin karatunta, sai Sarkin na Gaya ya sa aka zo da yarinyar da kuma iyayenta har gabansu.

    Nan take wakilin a Ma’aikatar Ilimi ta jihar Kano, Malam Haruna Mohammed Pandau, ya ba Saratu kayan makaranta da jakar makaranta da kuma wasu kayayyakin karatu.

    Shi kuma Ado Tafida Zango, mai kula da shirin AGILE a jihar, ya ba ta Naira 20,000 daga aljihunsa don taimaka wa karatun nata.

    Muna fatan Allah ya kara bawa yaranmu nasara.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.