• Thu. Mar 28th, 2024

Amihad.com

Number 1 Financial Education and Tech Blog

Duniya Ina Zaki Damu: Cikin Dare An Dauko Bidiyon Abubuwa Da Matan Hausawa Sukeyi A Gidan Gala

ByLucky Murakami

Oct 23, 2022

Wani abin da zai baka takaici kuma shi ne, Gidan Dirama ba gida ne da tsofaffin karuwai ke kwana ba, a a duk wacce ka gani in ma dai budurwa ce ta baro gidan iyayenta, ko kuma a a bazawara ce mai kuruciya da idan ba ta gaya maka ba ba za ka san sirrinta.

A halin yanzu mafi aksarinsu ba suna baro gida ne domin za a yi musu auren dole kamar a da can ba, a a suna fita ne domin sun fi karfin iyayensu su fada musu su ji, wasu ma suna fita ne da izinin iyayen domin su iyayen sun san ko da sun fada ba za su ji ba.

Wakilimmu ya samu zantawa da wata uwar ‘ya’ya uku ‘yan mata biyu da namiji daya da ta nemi a sakaya sunanta, wadda daya daga cikin ‘ya’yan nata ta fita zuwa irin wannan gida na Dirama, inda ta bayyana masa cewa, ita ce ta bar yarinyar zuwa wannan gida.

“Gaskiya ni ce nake barinta ta je don kai na, dalili kuwa shi ne, gara dai ko me za ta yi nasan tana dawo wa gida ai zan san halin da take ciki fiye da a ce ta fita ina fushi da ita, kuma ta ki dawowa gida.

“Ka san yaron yanzu ka haife shi ne amma ba ka haifi halinsa ba, ai ina nan zaune take kawo min labarin wasu suna shafe shekara da shekaru ba su dawo gida ba. Ita dai ‘yar uwarta ka ga tana zuwa makaranta ta addini da ta Boko amma dai ita waccan mu nan muna ta addu’a Allah ya shirya mana, na yi kuka a farkon lamarin har na hakura sai dai‘yar uwarta ta ce ba ni hakuri, amma dai ban taba yi mata baki ba,”in ji ta.

To ko yaya ‘yan uwan irin wadannan‘yan mata ke ji a ransu yayin da aka ce ‘yar uwarsu ta shiga irin wannan yanayi? Aminu wa ne ga ita wannan yarinya, ya bayyana wa wakilimmu irin halin da ya tsinci kansa lokacin da ya shigo ya samu mahaifiyarsu na kuka.

“Hankalina ya yi matukar tashi da na shigo gida na samu ummanmu tana kuka, abin da ban saba gani ba, da na tambayi daya kanwar tamu ta fada min abin da yake faruwa, na ji kamar raina zai fita, ana cikin haka sai ga ta ta shigo,babarmu ba ta taba hana ni abu na ki ba amma a ranar da fara dukanta ban ma san tana cewa na bari ba, kuma daga ranar har yanzu ba na yi mata Magana idan ta zo gida,” in ji shi.

By Lucky Murakami

A savant on system network security and information technology with adept leadership skills.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *