Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    Gorin Rashin Haihuwa Akayi Mun Shiyasa Na Saci Jariri Inji Ɓarauniyar Da Aka Kama A Bauchi

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 29, 2022No Comments1 Min Read

    Jami’an tsaro sun kama wata mata da ake zargin ta saci jariri sabuwar haihuwa, Ibrahim Khalid a asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi.

    Jaridar Punch ta ce jaririn wanda ɗan tagwaye ne, an sace shi ne ranar Talatar makon jiya a dakin asibiti, kafin a gano tare da mayar da shi hannun mahafiyarsa.

    Ana zargin wacce ta saci jaririn da yin shiga kamar ma’aikaciyar jinya a asibitin kuma ta lallaba ta zari yaron ba tare da an kama ta ba.

    Bayanai sun ce wadda ake zargin ta sace jaririn ne saboda damuwar da ta shiga sakamakon yawan gorin da dangin miji ke yi mata na rashin haihuwa.

    Wadda zargin ta kai jaririn kauyensu na Dull a cikin karamar hukumar Tafawa Balewa tana cewa dan da ta haifa ne.

    Da a ke tuhumar ta, sai matar ta kada baki ta ce ta na shan horon rashin haihuwa ne shi ya sanya ta aikata wannan aika-aika.

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.