AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Haryanzu Babu Namijin Da Yazo Mun Da Maganar Aure, Wata Jaruma Ta Koka Kan Rashin Mijin Aure
    Entertainment

    Haryanzu Babu Namijin Da Yazo Mun Da Maganar Aure, Wata Jaruma Ta Koka Kan Rashin Mijin Aure

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiNovember 17, 2022No Comments3 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Wata matashiyar jarumar fim ta bayyana cewa babu wani namiji da ya taɓa tunkararta da maganar aure, kuma dama tana ganin cewa har yanzu bata kai munzalin da zata yi aure ba.

    Jarumar tana Sakandire ta fara harkar fim
    Sharon Ifedi jarumar fim ce dai ta kudancin Najeriya wacce ta fara taka leda a harkar wasan kwaikwayo tun a lokacin da take a sakandire. Sai dai tana ganin kamar har yanzu shekarun ta basu kai ba na wanda za’a ce tayi aure.

    A wata tattaunawa da majiyar mu ta samu, jarumar tace a can baya tayi ƙudurin ta karanci ɓangaren aikin likitanci ne kafin daga bisani kuma ta tsinci kanta a harkar fina-finai.

    Da aka tambaye ta ko an taɓa yi mata tayin aure ba ta amsa ba a waɗannan shekarun nata? Jarumar ta bayyana cewa bata taɓa ba, sabili da a cewar ta babu wani wanda ya taɓa tunkararta da maganar cewa yana son ya aure ta.

    Tafi maida hankali kan harkokin fim
    Jarumar ta ƙara da cewar dangane da kuma irin namijin da take so, wannan idan lokacin da take ganin ta isa aure yayi zata duba ta gani, tunda a yanzu dai bata san komai ba dangane ga maza.

    Ta kuma ƙara da cewar yanzu tafi maida hankali kan sana’ar ta ta fim. Bata alaƙa ko soyayya da kowa. Duk da dai ta tabbatar da cewa akwai mazaje da dama da suke son ta.

    Da aka tambayi jarumar kan ko wane irin ƙalubale ne take fuskanta a harkokin ta na wasan kwaikwayo a matsayin ta na jaruma mai ƙaranci shekaru. Jarumar ta bayyana cewa abinda ke takura mata shine, yanayin yadda take baro ‘yan uwanta a gida tun da sassafe ta tafi wajen ɗaukar fim, ba zata dawo ba a wasu lokutan ma sai dare.

    Sai dai tace babban ƙalubalen da a yanzu take fuskanta sune sauran matakan da bata taɓa fitowa ba a cikin finafinan da take yi. Tace a matsayin jaruma yana dakyau ace mutum ya iya fitowa a matakai da dama.

    Wani ya taɓa rungume ta a tsakiyar jama’a

    Ta bayyana cewa wani abu kuma da yakan ɓata mata rai shine yadda wasu daga cikin masoyanta ke yi mata a yayin da suka ganta. Tace akwai lokacin da wani daga cikin masoyanta ya taɓa zuwa ya rungume ta a wajen wani taro da har sai da mutane suka janye shi daga jikin ta.

    Daga ƙarshe ta bawa jarumai mata masu tasowa shawara kan su riƙa ƙoƙarin baiwa kansu atisayen fitowa a fim kafin ma suje gaban furodusa. Tace hakan zai taimaka musu sosai.

    A wani labarin na daban kuma, kunji Yadda wata matashiyar mata ta kashe ɗan cikin ta da ta haifa.

    Wata mata ‘yar shekara 18 dake yankin Olocha-Adogba da ke ƙaramar hukumar Awgu ta kashe ɗan jaririn da ta haifa ta hanyar soka masa wuƙa da tayi.

    Majiyar mu ya premium times ta wallafa cewa matar mai suna Joy Okonkwo tayi amfani da wuƙa ne wajen caka ma jaririn nata jim kaɗan bayan haihuwar shi a gida. Mummunan lamarin dai ya faru ne a ranar Litinin data gabata da misalin ƙarfe ɗaya na rana.

    Ance wannan ɗanyan aiki dai da ta aikata ya samo asali ne dai daga shawarar da ake tunanin mahaifiyar matar ‘yar shekara 60 mai suna Christiana Okonkwo ta bata.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Uba Ya Hada Baki Da Abokinsa Sun Yiwa Yarsa Fyade

    November 26, 2022

    Kalli Bidiyon Sabuwar Rawar Da Safara’u Tayi Wanda Ta Jawo Mata Matsala Wajen Mutane

    November 24, 2022

    Kalli Abinda Mutane Suka Yiwa Hamisu Breaker Lokacin Da Ya Kaiwa Mahaifiyarsa Ziyara

    November 21, 2022

    Bidiyon Yadda Amarya Taki Sumbatar Ango A Gaban Jama’a Saboda Yana Warin Baki

    November 17, 2022

    Kalli Abinda Jaruma Momee Gombe Da Wani Jarumi Sukayi A Gidan Gala Ko Kunya Babu

    November 15, 2022

    Kalli Abinda Wani Saurayi Ya Yiwa Budurwa A Idon Jama’a Ko Kunya Babu

    November 11, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.