AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Jerin Jihohi Takwas Da Suka Riƙewa Ma’aikata Albashin Aƙalla Watanni Shida
    News

    Jerin Jihohi Takwas Da Suka Riƙewa Ma’aikata Albashin Aƙalla Watanni Shida

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 23, 2022No Comments4 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Labarin da muka tattaro daga jaridar Premium Times ya kawo cewa Jihohi takwas sun yi mirsisi sun ƙi biyan ma’aikatan su albashin aƙalla watanni shida. Wani rahoto ne ya tabbatar da haka.

    Jihohin sun haɗa da Taraba, Edo, Ebonyi, Ondo, Filato, Imo, da Abiya. Rahoton ya ce sun ƙi biyan ma’aikata albashin kuma sun kasa biyan ‘yan fansho haƙƙoƙin su.

    Kungiyar BudgIT ce ta fitar da rahoton inda ta ce aƙalla jihohi 12 a cikin jihohin Najeriya 36 ba su biya aƙalla albashin wata ɗaya ko sama da haka ba ya zuwa 28 Ga Yuli, 2022.

    Jihar Abiya ba ta biya wasu daga cikin ma’aikatan jihar albashi ba tsawon watanni 22.

    “Jihar Abiya ta kasa biyan albashin ma’aikatan manyan makarantun gaba da sakandare tsawon watanni shida, yayin da Jihar Ebonyi ba ta biya haƙƙin ‘yan fansho na tsawon watanni shida ba.” Inji BudgIT.

    Rahoton ya nuna ma’aikatan sakateriyar Jihar Taraba sun koka kan yadda ake masu tsallaken watanni wajen biyan albashin aƙalla tsawon watanni shida. Su kuma malamai a manyan makarantun jihar Ondo da jami’an unguwar zoma na asibitin jihar Ondo ba a biya su albashin watanni huɗu ba.

    Wani ma’aikatacin gwamnatin Jihar Ondo ya shaida wa wakilin mu cewa su na cikin wani mawuyacin hali. “Ana biyan mu albashi a baya. Amma rabon da a biya mu tun cikin watan Fabrairu, 2022. Daga watan Maris zuwa yanzu ko sisi ba a biya mu ba.” Inji ma’aikaciyar.

    Sai dai Kwamishinan Ilmin Jihar Ondo, Bamidele Olateju, ya ce daga watan Afrilu ne ba a sake biya ba zuwa yanzu.

    “An riƙa biyan albashi har zuwa watan Afrilu. Amma daga nan ne ba a sake biya ba. Amma muna bakin ƙoƙarin an biya na sauran watannin da su ka rage.” Haka ya shaida wa wakilin mu a ranar Juma’a.

    Jaridar ta Premium Times ta tuntuɓi jihohin da su ka ƙi ko su ka kasa biyan albashin ma’aikatan su.

    Jihohi takwas sun riƙe wa ma’aikata aƙalla albashin watanni shida.

    Jihohi takwas sun yi mirsisi sun ƙi biyan ma’aikatan su albashin aƙalla watanni shida. Wani rahoto ne ya tabbatar da haka.

    Jihohin sun haɗa da Taraba, Edo, Ebonyi, Ondo, Filato, Imo, da Abiya. Rahoton ya ce sun ƙi biyan ma’aikata albashin kuma sun kasa biyan ‘yan fansho haƙƙoƙin su.

    Kungiyar BudgIT ce ta fitar da rahoton inda ta ce aƙalla jihohi 12 a cikin jihohin Najeriya 36 ba su biya aƙalla albashin wata ɗaya ko sama da haka ba ya zuwa 28 Ga Yuli, 2022.

    Jihar Abiya ba ta biya wasu daga cikin ma’aikatan jihar albashi ba tsawon watanni 22.

    “Jihar Abiya ta kasa biyan albashin ma’aikatan manyan makarantun gaba da sakandare tsawon watanni shida, yayin da Jihar Ebonyi ba ta biya haƙƙin ‘yan fansho na tsawon watanni shida ba.” Inji BudgIT.

    Rahoton ya nuna ma’aikatan sakateriyar Jihar Taraba sun koka kan yadda ake masu tsallaken watanni wajen biyan albashin aƙalla tsawon watanni shida. Su kuma malamai a manyan makarantun jihar Ondo da jami’an unguwar zoma na asibitin jihar Ondo ba a biya su albashin watanni huɗu ba.

    Wani ma’aikatacin gwamnatin Jihar Ondo ya shaida wa wakilin mu cewa su na cikin wani mawuyacin hali. “Ana biyan mu albashi a baya. Amma rabon da a biya mu tun cikin watan Fabrairu, 2022. Daga watan Maris zuwa yanzu ko sisi ba a biya mu ba.” Inji ma’aikaciyar.

    Sai dai Kwamishinan Ilmin Jihar Ondo, Bamidele Olateju, ya ce daga watan Afrilu ne ba a sake biya ba zuwa yanzu.

    “An riƙa biyan albashi har zuwa watan Afrilu. Amma daga nan ne ba a sake biya ba. Amma muna bakin ƙoƙarin an biya na sauran watannin da su ka rage.” Haka ya shaida wa wakilin mu a ranar Juma’a.

    Kazalika jaridar ta tuntuɓi jihohin da su ka ƙi ko su ka kasa biyan albashin ma’aikatan su.

    Wannan matsala ta zama ruwan dare a jihohi da dama, har ta sa wasu ma’aikatan yanzu sun fantsama yin wasu ƙananan sana’o’in rufa wa kai da iyali asiri.

    Yayin da ɗawainiyar ciyar da iyali ta sha kan su, wasu sun koma ƙananan kasuwanci, haya da baburan okada, tuƙin taksi ko dillancin kayayyaki musamman mata a cikin gidaje da kasuwanni.

    Haka kuma da yawa sun kama kiwon dabbobi, kiwon kifi da kiwon kaji.

    Related

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.