Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    Jerin Jihohi Takwas Da Suka Riƙewa Ma’aikata Albashin Aƙalla Watanni Shida

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 23, 2022No Comments4 Mins Read

    Labarin da muka tattaro daga jaridar Premium Times ya kawo cewa Jihohi takwas sun yi mirsisi sun ƙi biyan ma’aikatan su albashin aƙalla watanni shida. Wani rahoto ne ya tabbatar da haka.

    Jihohin sun haɗa da Taraba, Edo, Ebonyi, Ondo, Filato, Imo, da Abiya. Rahoton ya ce sun ƙi biyan ma’aikata albashin kuma sun kasa biyan ‘yan fansho haƙƙoƙin su.

    Kungiyar BudgIT ce ta fitar da rahoton inda ta ce aƙalla jihohi 12 a cikin jihohin Najeriya 36 ba su biya aƙalla albashin wata ɗaya ko sama da haka ba ya zuwa 28 Ga Yuli, 2022.

    Jihar Abiya ba ta biya wasu daga cikin ma’aikatan jihar albashi ba tsawon watanni 22.

    “Jihar Abiya ta kasa biyan albashin ma’aikatan manyan makarantun gaba da sakandare tsawon watanni shida, yayin da Jihar Ebonyi ba ta biya haƙƙin ‘yan fansho na tsawon watanni shida ba.” Inji BudgIT.

    Rahoton ya nuna ma’aikatan sakateriyar Jihar Taraba sun koka kan yadda ake masu tsallaken watanni wajen biyan albashin aƙalla tsawon watanni shida. Su kuma malamai a manyan makarantun jihar Ondo da jami’an unguwar zoma na asibitin jihar Ondo ba a biya su albashin watanni huɗu ba.

    Wani ma’aikatacin gwamnatin Jihar Ondo ya shaida wa wakilin mu cewa su na cikin wani mawuyacin hali. “Ana biyan mu albashi a baya. Amma rabon da a biya mu tun cikin watan Fabrairu, 2022. Daga watan Maris zuwa yanzu ko sisi ba a biya mu ba.” Inji ma’aikaciyar.

    Sai dai Kwamishinan Ilmin Jihar Ondo, Bamidele Olateju, ya ce daga watan Afrilu ne ba a sake biya ba zuwa yanzu.

    “An riƙa biyan albashi har zuwa watan Afrilu. Amma daga nan ne ba a sake biya ba. Amma muna bakin ƙoƙarin an biya na sauran watannin da su ka rage.” Haka ya shaida wa wakilin mu a ranar Juma’a.

    Jaridar ta Premium Times ta tuntuɓi jihohin da su ka ƙi ko su ka kasa biyan albashin ma’aikatan su.

    Jihohi takwas sun riƙe wa ma’aikata aƙalla albashin watanni shida.

    Jihohi takwas sun yi mirsisi sun ƙi biyan ma’aikatan su albashin aƙalla watanni shida. Wani rahoto ne ya tabbatar da haka.

    Jihohin sun haɗa da Taraba, Edo, Ebonyi, Ondo, Filato, Imo, da Abiya. Rahoton ya ce sun ƙi biyan ma’aikata albashin kuma sun kasa biyan ‘yan fansho haƙƙoƙin su.

    Kungiyar BudgIT ce ta fitar da rahoton inda ta ce aƙalla jihohi 12 a cikin jihohin Najeriya 36 ba su biya aƙalla albashin wata ɗaya ko sama da haka ba ya zuwa 28 Ga Yuli, 2022.

    Jihar Abiya ba ta biya wasu daga cikin ma’aikatan jihar albashi ba tsawon watanni 22.

    “Jihar Abiya ta kasa biyan albashin ma’aikatan manyan makarantun gaba da sakandare tsawon watanni shida, yayin da Jihar Ebonyi ba ta biya haƙƙin ‘yan fansho na tsawon watanni shida ba.” Inji BudgIT.

    Rahoton ya nuna ma’aikatan sakateriyar Jihar Taraba sun koka kan yadda ake masu tsallaken watanni wajen biyan albashin aƙalla tsawon watanni shida. Su kuma malamai a manyan makarantun jihar Ondo da jami’an unguwar zoma na asibitin jihar Ondo ba a biya su albashin watanni huɗu ba.

    Wani ma’aikatacin gwamnatin Jihar Ondo ya shaida wa wakilin mu cewa su na cikin wani mawuyacin hali. “Ana biyan mu albashi a baya. Amma rabon da a biya mu tun cikin watan Fabrairu, 2022. Daga watan Maris zuwa yanzu ko sisi ba a biya mu ba.” Inji ma’aikaciyar.

    Sai dai Kwamishinan Ilmin Jihar Ondo, Bamidele Olateju, ya ce daga watan Afrilu ne ba a sake biya ba zuwa yanzu.

    “An riƙa biyan albashi har zuwa watan Afrilu. Amma daga nan ne ba a sake biya ba. Amma muna bakin ƙoƙarin an biya na sauran watannin da su ka rage.” Haka ya shaida wa wakilin mu a ranar Juma’a.

    Kazalika jaridar ta tuntuɓi jihohin da su ka ƙi ko su ka kasa biyan albashin ma’aikatan su.

    Wannan matsala ta zama ruwan dare a jihohi da dama, har ta sa wasu ma’aikatan yanzu sun fantsama yin wasu ƙananan sana’o’in rufa wa kai da iyali asiri.

    Yayin da ɗawainiyar ciyar da iyali ta sha kan su, wasu sun koma ƙananan kasuwanci, haya da baburan okada, tuƙin taksi ko dillancin kayayyaki musamman mata a cikin gidaje da kasuwanni.

    Haka kuma da yawa sun kama kiwon dabbobi, kiwon kifi da kiwon kaji.

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.