• Wed. Jan 15th, 2025

Amihad.com

Number 1 Financial Education and Tech Blog

Kotu Ta Umarci Wani Ma’akacin Gwamnati Ya Dawo Da Albashinsa Na Shekara Goma Sha Daya

ByLucky Murakami

Aug 8, 2022

Abun mamaki baya karewa a wannan rayuwa inda wata babban kotu a jihar Filato ta umarci wani babban ma’aikacin cibiyar nazarin lafiyar dabbobi ta kasa (NVRI) da ke Vom a jihar Filato, Muhammed Nasiru, da ya amayo albashin shekara 11 da ya amsa a matsayin babban jami’in sashin mulki na NVRI.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Christy Dabup, ya samu Nasiru ne da laifin da ake zarginsa tare da yanke masa hukuncin zaman gidan yari na wata bakwai ko zabin biyan tara na N150,000.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ce ta gurfanar da Nasiru a gaban kotun bisa tuhume-tuhume guda biyu da suka hada da bayyar da takardun karya da kasa iya gabatar da sahihin takardun neman aiki da cibiyar nazarin lafiyar dabbobi ta NVRI.

ICPC ta ce Nasiru bai cancanci samun damar daukar aiki ba bisa dalilin cewa an taba masa ritayar dole a cibiyar kula da harkokin shari’a ta kasa da ke Abuja (NJI) a shekarar 2003.

Bayan da kotun ta kama wanda ake zargin da aikata manyan laifuka, ta umurce shi da ya dawo da albashin shekara 11 da ya karba wa hwamnatin tarayya kuma zai shafe watanni bakwai a daure.

Alkalin kotun da yake yanke hukunci, ya ce Lauyan ICPC, Evans Peter, ya iya gamsar da kotun kan zarge-zargen da suke yi ma wanda suke kara, a yayin da kokarin kariya na Muhammed Nasiru suka gaza kare kansu.

 

Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin Da Muke Ciki a Yanzu

“Ku tashi mu farka ‘yan Arewa Ku san bacci aikin kawai ne” in ji Marigayi Dakta Alhaji Mamman Shata Katsina.

Wannan shi ne baitin wakar da marigayi Alhaji Dakta Mamman Shatan Waka, Shata Katsina mawakin Arewa ya yi domin tunasar da mu abin da ya kamata mu yi a matsayin mu na ‘yan Nijeriya ya kamata mu sani, to yanzu an wayi gari Arewa na cikin yanayin dimuwa da tashin hankali a kan yadda Nijeriyarmu ke tafiya a matakin rashin tsaro da rashin sanin makomar kasar a kakar zaben 2023 da ke fuskantowa, talaka da masu hannu da shuni da mahukuntan kasar ba mu da wata kasa da muke alfahari da ita tamkar wannan kasar.

Shin me ya sa talaka zai zuba ido a kan wani abin da bai taka kara ya karya ba ko kuma a ce wasu ‘yan canjin Nairori da za a bashi a yayin zabe ya kuma bayar da kasar tamu ta gado ga hannun ‘yan jari hujja wadanda su ba kasar ce a gabansu ba.

Idan ba a manta ba, a lokacin da jam’iyyar APC ke babban gangaminta na farko a Abuja a kafin zaben shekarar 2015, Audu Ogbe ya hau Mimbari ya shelanta wa talaka cewa ‘BringBackOurGirl,’ kungiyarsu ce, kuma suna goyon bayan abubuwan da take.

Yau kuma an wayi gari ita dai jam’iyyar ta APC ta ki amincewa da duk wata kungiya ko wasu gungun al’umma da za su fito domin su nuna ranshin goyon ko rashin jin dadin tsarin mulkin da take gudanarwa a Nijeriya.

By Lucky Murakami

A savant on system network security and information technology with adept leadership skills.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *