AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Miji Ya Kashe Matarsa Saboda Ta Shanye Masa Koko
    News

    Miji Ya Kashe Matarsa Saboda Ta Shanye Masa Koko

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 11, 20221 Comment4 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Wani magidanci ya kashe matarsa saboda sabanin da suka samu a kan koko a Jihar Neja.

    Majiyoyi daga kauyen Kadaura na Karamar Hukumar Rafi a Jihar sun ce matar ta bakunci lahira ne bayan mijin nata mai shekara 20 ya lakada mata duka, ta yanke jiki ta fadi magashiyyan nan take rai ya yi halinsa.

    Kakakin ’yan sanda a Jihar Neja, DSP Wasiu Abiodun, ya ce, “Wanda ake zargin ya amsa cewa ya yi matar tasa duka saboda dan sabanin da suka samu a kan koko.

    “Nan take ta fadi magashiyyan, aka dauke ta ranga-ranga zuwa Babban Asibitin da ke garin Wushishi inda likitoci suka tabbatar cewa rai ya yi halinsa.”

    Kakakin ’yan sandan ya kuma tabbatar wa Aminiya cewa ’yan sanda na tsare da matashin magidancin a Babban Ofishinsu da ke garin Kagara, suna masa tambayoyi.

    “An riga an fara bincike kuma da zarar an kammala za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu,” inji DSP Wasiu Abiodun.

    Labarin kisan na zuwa ne mako guda bayan wani makamancinsa inda ake zargin wata matar aure da lakada wa kishiyarta duka da muciya har ta mutu, sannan ta kona gawarta.

     

    Yadda Uba Ya Kashe Dansa A Kano

    Ana zargin wani mahaifi da lakada wa dansa dukan da ya yi ajalinsa saboda zargin satar masa kaya a shagonsa na kasuwanci.

    Rundunar ’yan sanda a jihar Kano ce ta tabbatar hakan da kuma kama wanda ake zargin.
    Mai magana da yawun Rundunar, DSP Abdullahi Kiyawa, ya ce mamacin mai shekara 19 ya rasu ne bayan mahaifinsa ya lakada masa duka a daren ranar Juma’ar da ta gabata.

    Mahaifin nasa ya yi masa dukan ne bisa zargin dan da satar galan biyu na manja a kantinsa.

    A ranar Litinin ce matashin ya ce ga garinku yayin da yake jinyar dukan da mahaifin nasa ya yi masa a Asibitin Kwararru na Murtala Mohammed da ke kwaryar birnin Kano.

    Shaidu sun ce suna zaune a shagonsu sai suka ga mahaifin mamacin yana dukan sa.

    “Muna zaune a bakin shagonmu, sai muka ji yana duka yaronshi a cikin shago.

    “Amma ba mu da masaniya a kan musabbabin duka yaron kuma ganin cewa abu ne tsakanin uba da dansa ya sanya ba mu tanka masa ba.

    “Sai daga baya wani makwabcinsa mai wankin hula ya nemi shi ga tsakani amma mahaifin ya daka masa tsawa cewa ya fitar masa daga shago.

    “Ganin haka ya sanya muka koma gefe muka zama ’yan kallo,” inji Kabiru.

    Ita kuwa mahaifiyar yaron, wacce ta rabu da mahaifinsa tsawon lokaci, ta ce ganin karshe da ta yi wa dan nata shi ne lokacin da ta kai shi asibiti bayan da ya zo gidan mijinta a unguwar Danbare cikin wani mawuyacin hali.

    “Kawai sai ganin sa na yi a gefe na a kwance, na ce Abba mai ya same ka, sai cewa ya yi babanmu ne ya dake ni.

    “Na ce mai ka yi masa, sai ya ce wai mansa ne bai gani ba guda biyu kuma na rantse masa da Allah ba ni na dauka ba amma ya kama ni da duka.

    “Sai na ce yanzu me ke damun ka, sai ya ce kansa ne yake masa ciwo domin a ka ya dake shi,” inji mahaifiyarsa.

    DSP Kiyawa ya kara da cewa, mahaifin a yanzu yana hannunsu inda ake ci gaba da gudanar da bincike.

    “Yanzu yana hannunmu, kuma Kwamishinan ’Yan sandan Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko ya sa a dawo da shi sashen manyan laifuka a nan Hedikwatarmu da ke Bompai.

    “Dole sai muna kai zuciyarmu nesa, duk inda aka ce yau ka na tare da wani an samu sabani, a daina kai duka ko da kuwa da hannu ne, saboda ba’a san mai zai faru ba,” in ji DSP Kiyawa.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Pingback: Yadda matashi ya halaka matarsa saboda ta shanye masa Koko | Labarun Hausa

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.