AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Nasan Yadda Zan Gano Da Kuma Magance Matsalolin Nigeria – Bola Tinubu
    News

    Nasan Yadda Zan Gano Da Kuma Magance Matsalolin Nigeria – Bola Tinubu

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 5, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatin da zai kafa idan ya ci zaɓen 2023, za ta ƙunshi zaƙaƙuran mutanen da za su yi hangen nesan gano matsalolin da ƙasar nan ke fama da su, tare da magance su nan da nan.

    Tinubu ya yi wannan bayani a Abuja ranar Asabar, lokacin da aka ƙaddamar da motoci masu ɗauke da tambarin kamfen na Gida-gida, wato “Door-to-Door Tinubu/Shettima 2023”, wanda ƙungiyar Kakakin Majalisar Dokokin Jihohin Arewa na APC su ka shirya.

    Tinubu ya ce sannan kuma tawagar sa na da hazaƙar azurta Najeriya da ‘yan ƙasa baki ɗaya.

    “Ai mu ne masu hangen nesan cikin jam’iyya. Mu na son ilmi mai inganci ga ‘ya’yan mu, mu na buƙatar ci gaban Najeriya da arzikin ƙasa musamman ta hanyar bunƙasa harkokin noma ta hanyar dabarun zamani.

    “Mu na ji da kan mu cewa za mu iya. Mu na da abin da ake buƙata wajen masu irin wannan ƙoƙari da kishi. Mu na da wannan ƙudiri. Kuma mu na da wannan juriyar iya yin aikin.” Inji Tinubu.

    Ya ƙara da cewa APC ba ta damu da PDP ba, ballantana ma ta tsaya ta na ce-ce-ku-ce da ita ba.

    Ya ce a matsayin APC na jam’iyyar da ta ƙunshi masu tunani, ba ta buƙatar ɓata lokacin yin hayaniya da PDP, jam’iyyar da rigimar shugabanci ma kaɗai ya ishe ta.

    “Kada mu riƙa surfa wa jam’iyyun adawa zagi. Ai mun fi su sanin ya-kamata. Mun fi su basira da nagarta. Ta mu ba irin ta su ba ce.

    “Sun yi shekaru 16 su na mulki, amma a lokacin sun manta cewa akwai buƙatar jiragen ƙasa masu jigilar jama’a da kayan su a ƙasar nan.” Inji Tinubu.

    Daga nan ya shawarci PDP cewa ta jira ta ga irin kayarwar da APC za ta yi mata a ranar zaɓen shugaban ƙasa.

    Haka kuma Tinubu ya gode wa ƙungiyar ‘yan Majalisar Dokokin Arewa dangane da wannan yunƙurin haɗa kayan kamfen da su ka fara yi masa.

    “Kun sauƙaƙa mana rayuwa, saboda ko sisi ba ku nema a wurin mu ba. Lallai ku ma ku na neman ganin Najeriya ta zama ƙasaitacciyar ƙasa.

    Shi ma mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa Kashim Shettima, ya ce idan aka zaɓi Tinubu, za su gina sabuwar Najeriya.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.