AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Ni Shahararren Dan Tsibbu Ne Kafin Na Shiga Izalah – Sheikh Bello Yabo Sokoto
    News

    Ni Shahararren Dan Tsibbu Ne Kafin Na Shiga Izalah – Sheikh Bello Yabo Sokoto

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 14, 2022Updated:August 14, 2022No Comments4 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Kamar yadda mukayi karo da wani bidiyo inda babban malami Bello Yabo ya bada wani labari wanda ya shafi rayuwarsa wanda ya kira abun da tsoron labari amma karatu ya biyo ta wajen yasa ya bada wannan labari.

    Kafin mu shiga cikin wannan jawabi da zamu gabatar muku da bidiyonsa a kasa yana dakyau ku san cewa amihad.com ta tattara wannan bayanai badan cin mutunci ko batawa wani suna ba.

    Na daga cikin dalilan dayasa muka kawo wannan rahoto shine muhimmancin tuba ga Allah idan an aikata wani lafi ko kuskure wanda ya sabawa dokar Allah. Hakika ubangiji ya kira kansa da shi mai yafiya ne ga ko wane laifi da akayi masa in har anbi sharudan tuba.

    Shiyasa muka kawo muku wannan labari domin tuni ga yan uwa musulmai akan yawan istigfari ga ubangijin halitta musammam a al’amuran rayuwar yau data kasance a na yawan aikata laifuffuka iri iri wanda suka sabawa wa dokar ubangiji.

    Kazalika amihad.com ta kawo wannan labari da malam Bello Yabo ya bayar cikin bidiyon karatun daya gabatar a baya. Kuma sanin kowa ne malam ya bada wannan labari a matsayin laifi da yayi a baya kuma ya tuba a yanzu domin babu abinda yake cikin harkar tsibbu illa karya da yaudara kuma dukkaninsu manyan laifuka ne wajen mahalicci.

    A cikin bidiyon da amihad.com zata kawo muku a kasa zakuji yadda mallam Bello Yabo yake cewa:

    “Kafin mu shiga izalah, is an old story ai kasan munyi tsibbu ko, munyi tsibbu hmm!, Allah ya gafarta mana” Inji malam bello yabo

    Malamin yace ba abinda ke cikin harkar tsibbu illa karya da yaudara kuma duk wani irin wannan harka ba’a rabashi da wadannan abubuwa.

    Ya kuma bada labarin yadda aka kawo masa wani dan shaye shaye yayi masa magani inda ya kulleshi a daki ba abinda yayi masa amma saboda ya hanashi kayan shaye shaye hakan yasa yaron ya dawo hayyacinsa.

    Bayan ya kammala wanan aiki ake tayi masa godiya bisa ceto rayuwar wannan yaro wanda a gaskiya kuma ba abinda yayi masa, koda kuwa addu’a baiyi masa ba.

    Gadai bidiyon nan a kasa don ji ta bakin malam domin tabbatarwa da kanku.

    https://amihad.com/wp-content/uploads/2022/08/Ni-Shahararren-Dan-Tsibbu-ne-Kafin-In-Shiga-Izala.mp4

    Da fatan kun amfana da wannan labari kada ku kosa kuyi kasa domin karanta yadda ta kasance tsakanin malam bello yabo da malam murtala bello sokoto.

    Rikici Ya Barke Tsakanin Sheikh Bello Yabo Da Mallam Murtala Bello Sokoto Akan Yan Siyasa

    A wani labari da muka kawo muku a nan ya nuna yadda rikici ya barke tsakanin malaman

    A cikin wani bidiyo da mukai karo dashi cikin karatun Mallak Murtala Bello Sokoto yayi magana akan maganganu marasa dadi da Sheikh Bello Yabi yayi akansa inda shima ya mayar masa nasa martanin.

    Inda ya fara da cewa zagi ba tarbiyar Annabi bace kuma ya karyata masu cewa Manzon Allah yana zagi a lokacin rayuwarsa, bayan an zagi shi Malam Murtala Bello. Inda yace yace wanda ya fara wannan zagi shine azzalumi kuma shi bazai rama ba.

    Malam Murtala Bello Sokoto ya zargi maganar da yayi akan yan takarar shugaban kasa Bola Tinubu da Atiku Abubakar ce ta jawo masa wadannan zage zage.

    Ya kuma kara da cewa tun daga shekarar 1999 zuwa 2019 tsohon malami ya nuna goyon bayansa ga wasu yan siyasa tun daga jihar sokoto har zuwa matakin shugaban kasa. Yaci mutuncin yan siyasa irinsu Attahiru Bafarawa, Alu Wammako, Aminu Waziri Tambuwal kuk saboda son abun duniya.

    Ya kuma kara da cewa malamin yayi karya da yace ya yiwa Buhari kamfen a shekarar 2015 da 2019, inda yace malamin baiyi Buhari ba a lokacin.

    Yace lokacin malamin yayima buhari kamfen shine a shekarar 2011 lokacin da yake kamfen da ayoyin bambancin musulmi da kafiri a matsayin shugaba.

    Kazalika ya kuma kara da cewa a lokacin Jonathan anyi zargin shi malamin (Sheikh Bello Yabo Sokoto) da kasancewa cikin malaman da sukaci kudin kamfen.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.