AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Sai Na Bawa Matata Kudi Take Yarda Na Kwanta Da Ita Wani Magidanci Ya Koka
    News

    Sai Na Bawa Matata Kudi Take Yarda Na Kwanta Da Ita Wani Magidanci Ya Koka

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiJuly 30, 2022Updated:August 27, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Wani magidanci ya nemi kotu ta raba aurensu saboda matarsa tana tatsarsa makudan kudade kafin ta amince ya yi mu’amalar auratayya da ita.
    Babbar Kotun Jihar Kwarra ta raba auren bayan sun shekara 28 da matarsa, wadda yake zargi da yawan kwartanci na wuce hankali.

    Magidancin ya shaida wa kotun cewa matar, “Takan shardanta mini ba ta cekin kudade masu tsoka, kafin ta yarda in kusance ta; idan ban ba ta ba kuma ba za ta amince ba kwata-kwata.”
    Ya shaida wa kotun cewa kwartoncin matarsa ya wuce misali, domin kwartayen nata na da yawa, kuma har ’ya’yanta take turwa karbar kudi daga wurinsu.

    “Har kwashe kayanta ta yi daga uwar dakanmu ta je ta tare a dakin saukar baki.

    “Ni kuma ba ta yarda in kusance ta sai idan na bata cekin makudan kudade, idan na ki kuma sai dai in hakura,” kamar yadda ya shaida wa kotu.

    Ya ce tsabar rashin kamun matar tasa ya sa ta yi watsi da nayin da ke kanta a matsayin matar aure.
    “Aurenmu ya riga ya rushe tunda har ta kai ga ni da ita ba ma iya zama mu tattauna abin da ya shafi rayuwarmu da ’ya’yanmu”, in ji shi.

    Lauyan mijin, Mista Josiah Adebayo, ya gabatar wa kotun hoton tsiraicin matar tare da saurayinta da aka samu a cikin wayarta a matsayin shaida.
    Don haka mijin ya bukaci kotu ta raba auren amma ta ba shi damar kula da ’ya’yan da tsakaninsu.

    Amma martaninta, Roseline ta musanta tuhumar da ake mata, sannan ta zargi mijinta da bin matan banza.

    Ta bayyana cewa ba ta kalubalantar bukatar mijin na kotu ta raba auren, amma tana so kotu ta mallaka mata wani bangare na gidansu da suke zama a Legas.

    A cewarta, ita da mijin ne suka yi hadaka wajen gina gidan.

    Da take yankiu hukunci, alkalin kotun, Mai Shari’a S.T Abdulqadri, ta amince da bukatar micin, tana mai cewa ta gamsu da shaidar da aka gabatar da ke tabbatar da zargin ke wa matar tasa.
    Ta kuma karyata ikirarin matar na hakki a gidansu na Legas, da take so a mallaka mata wani bangarensa.

    Amma kotun ba ta ba wa kowanne daga cikinsu hakkin riki yaran ba, saboda sun mallaki hankalin kansu, kowannensu ya fi shekara 20 da haihuwa.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.