AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Sheikh Daurawa Ya Bayyana Abinda Ummita Ta Fada Masa Kafin Saurayinta Dan China Ya Kasheta
    News

    Sheikh Daurawa Ya Bayyana Abinda Ummita Ta Fada Masa Kafin Saurayinta Dan China Ya Kasheta

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 19, 2022Updated:October 4, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya bayyana cikakken bayanin magana ta tsawon mintuna 15 da su ka yi da marigayiya Ummakulsum Buhari (Ummita) ta wayar tarho game da saurayinta, mako guda kafin rasuwar ta kamar yadda majiyarmu jaridar Daily Nigerian ta rawaito.

     

    Wani ɗan kasar China, mai suna Gheng Quanrong ne ya hallaka Ummita, bayan da ya caccaka mata wuƙa a gidansu da ke unguwar Janbulo a Kano.

    Da yake bayyana abinda su ka tattauna da marigayiyar a wani faifen bidiyo ds ke nuni da cewa a ɗaya daga cikin majalisin karatunsa ne, Daurawa ya ce ta kira shi ne domin neman shawara a kan mafita kan ƙudurin 5a na aurar ɗan China ɗin sabo da mahaifanta sun hana ta auren shi.

    “Na ce mata iyayenki su na da gaskiya saboda bai kamata nata ku riƙa auren wanda a ke da kokwanto a kan asalinsa,” in ji shi.

    Sai dai malamin ya ce ya bata shawarar ta gindaya wa masoyin na ta sharɗɗa biyar kafin su yi auren.

    “Sharadi na farko shi ne a tuntubi hukumar shige da fice ta ƙasa don tabbatar da ko da izini ya shigo ƙasar nan. Na biyu, a yi bincike kan aikin sa a Najeriya.

    “Na uku, na san Sarkin Kano ya naɗa sarkin ƴan China a Kano. Don haka a tambayi shugaban al’ummar kasar ko sun san shi, yankin da ya fito da kuma abin da yake yi?

    “Na huɗu, ya kamata kuma a sanar da ofishin jakadancin cewa ɗan kasar China na shirin auren ƴar Najeriya. Na biyar kuma na umarce ta da ta sanar da Hisbah don ta kara koya masa addinin musulunci, tunda ta ce min ya musulunta.

    “Ummita ta kara da cewa iyayensa a kasar China sun amince da auren, amma iyayenta sun ki amincewa da auren.

    “Amma na gaya mata idan kun cika waɗannan sharuɗɗa guda biyar, zan shawo kan iyayenki su yarda ki aure shi,” in ji shi.

    Daurawa ya ƙara da cewa addinin Musulunci ya amince da auren jinsi, yana mai cewa addinin ya kyamaci nuna wariyar launin fata, inda ya ƙara da cewa marigayiyar ta faɗa masa cewa ɗan China ɗin ya musulunta.

    Sheikh Daurawa ya kuma yi kira ga hukumomin da su ke da ruwa da tsaki da su tabbatar an hukunta ɗan China da ya kashe Ummita.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.