Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    Talakawa Ba Za Su Shiga Aljanna Ba – Inji Wani Minista

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 25, 2022No Comments3 Mins Read

    Wasu kalamai da wani babban dan siyasa yayi sun jawo magan ganu saboda tsaurin maganar kamar yadda mutane suka tabbatar

    Labarin da muke samu daga jaridar Aminiya ya shaida mana cewa Ministan Cikin Gida na Uganda, Mista Kahinda Otafire ya shiga cikin tsaka-mai-wuya sakamakon wasu kalaman da ya yi da ke nuna cewa talakawa ba za su shiga Aljanna ba.

    A cewar Ministan dai, talakawan ba za su Aljannar ba ne saboda sukar da suke yi wa Ubangiji wajen gabatar da korafe-korafe kowace rana.

    Ministan yayin jawabi ga wani taron dalibai a Kyenjojo, ya shaida musu cewa kada su zargi Ubangiji idan sun kasa amfani da damar da Ya ba su na yakar talauci, inda ya umarce su da su
    jajirce wajen samun arziki maimakon korafin da suke yi kowace rana.

    Mista Otafire ya ce kuskure ne mutane su rika gabatar da korafe-korafe
    da kuma zargin Ubangiji ba tare da tashi tsaye wajen yin ayyukan da za su samar musu da kudade ba.

    Ministan ya ce wannan hali na sukar Ubangiji da talakawa ke yi zai hana su shiga Aljanna.

    Wadannan kalamai sun haifar da ce-ce-ku-ce a kasar inda wadansu malaman addinai da kungiyoyi suke zargin gwamnati da gazawa wajen samar da yanayi mai kyau da talakawa za su samu sauki daga halin kuncin da suka samu kansu.

    Kasar Uganda na daya daga cikin kasashen da ke da dimbin matasan da ba su da ayyukan yi. (Rfi)

    Hukuma Tafara Bincike Akan Dan Sandan Daya Bindige Abokin Aikinsa Har Lahira

    Wani jami`in ‘Dan Sanda ya rasa ran sa bayan da bindigar abokin aikin sa ta tashi inda ta harbe shi, wanda ya rasu sanadin harbin da bindigar tayi masa a jihar Kano.

    Lamarin ya faru ne a unguwar Kurna a hanyar ‘Yan Sandan ta komawa jihar Katsina bayan sun kammala wani aiki da suka je yi jihar Kano.

    Sifiritandan ‘Yan Sanda, Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda shine kakakin rundar a jihar Kano ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai.

    “Akwai jami`an ‘Yan Sanda na jihar Katsina wanda suka zo aiki a nan jihar Kano, wanda kuma a unguwar Kurna suna cikin tafiya a motar su bindigar daya ta tashi inda kuma bayan ta tashi ta samu wani ‘Dan Sandan da yake cikin mota din, bayan wannan lamari an daukeshi da gaggawa an garzaya da shi asibiti inda likita ya tabbatar da cewa ya rasu,” in ji Kiyawa.

    Yanzu haka dai wannan ‘Dan Sanda da bindigar sa ta tashi wanda ya yi sanadiyar harbin wannan ‘dayan, wanda ya yi sanadiyar ran sa, an kama shi yana hannu, kuma an fara gudanar da bincike a kan wannan zargi na kisan kai.”

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.