AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Uwargida Ta Halaka Miji Daren Farko Da Zai Kwana A Dakin Amarya
    News

    Uwargida Ta Halaka Miji Daren Farko Da Zai Kwana A Dakin Amarya

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 29, 2022No Comments3 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Wani lamari me cike da mamaki wanda rundunar ’Yan sandan Jihar Nasarawa tana ci gaba da gudanar da bincike a kan wata mata da ake zargi da halaka mijinta ta hanyar daba masa wuka.

    Lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:00 na dare ranar Asabar da ta gabata a Unguwar Yarima da ke garin Marararaban Guruku a Karamar Hukumar Karu da ke iyaka da Abuja.

    Wata majiya a gidan ta shaida wa majiyar amihad.com cewa, wadda ake zargin mai suna Atika mai ’ya’ya 3 da marigayin mai suna Ibrahim Salihu mai shekara 37 da ke sana’ar kanikanci, ya je dakinta a daren don yi mata bankwana don wucewa dakin amarya inda takaddama ta shiga tsakaninusu.

    “Yakan yi kwana biyu a dakin kowace, sannan dabi’arsa ce yin sallama da wadda zai fita daga dakinta kafin ya koma dakin dayar.

    “Kuma haka ta kasance a ranar sai dai ana cikin haka sai ta cije shi a yatsa.”

    Mahaifiyar marigayin, Hajiya Hauwa Umar da ta je gidan bayan babban dan matar ya sanar da ita ta waya abin da ya faru da mahaifinsu, ta shaida wa Aminiya cewa bayanin da ta samu shi ne amaryar marigayin ta yi yunkurin ba shi agajin gaggawa ta hanyar daure masa yatsar da uwargidan ta ciza, sai dai ana cikin haka, sai uwargidan ta sake damkarsa ta baya, sannan ta daba masa wuka a wuya da ciki.

    Ta ce uwargidan wadda ta yi hakan bayan rufe kofar gidan, ta bi mijin nata da gora a lokacin da ya yi yunkurin gudu waje, lamarin da ya kai shi ga faduwa kasa, rai ya yi halinsa.

    Aminiya ta samu labarin cewa wani abin mamaki da ya sake aukuwa a lokacin da ake yunkurin kai marigayin asibiti, shi ne yadda wadda ake zargin ta rika ihu tana rungumar mijin tare da bukatar a taimaka mata cewa ta kashe mijinta.

    Wata majiya ta ce “Har ta yi yunkurin zama a babur din da aka dora shi a kai, amma sai aka ture ta gefe guda aka kai shi asibitin, inda a ka tabbatar ya rasu.”

    Aminiya ba ta samu jin ta bakin wadda ake zargin ba, sai dai wadansu makusantanta sun ce, ta jima tana korafi tare da zargin nuna fifiko ga amaryar daga bangaren mijin.

    “Ta ce ko taliyar Indomi ce ya sayo, sai ya ba wa kowacensu kwali daya duk da cewa uwargidan ’ya’yanta uku ne, ita kuma amarya a yanzu ne ta samu ciki.

    “Ko a daren da lamarin ya faru, amaryar ta fada wa mijin cewa tana son cin kifi, sai suka fita tare ya saya mata su ka dawo gida,” inji majiyar.

    Yunkurin jin ta bakin wani dan uwan marigayin ta waya mai suna Alhaji Sani Zangina, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Masu Harkar Fuloti a Karamar Hukumar Karu bai samu nasara ba.

    An yi jana’izar marigayin a safiyar Lahadin da ta gabata kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.