Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    Wadannan Sune Manyan Dalilan Dayasa Sanatoci Suke Kokarin Shige Buhari Daga Mulki

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 4, 2022Updated:August 4, 20221 Comment2 Mins Read

    Sanata mai wakiltar mazabar Bauchi ta arewa, Sanata Adamu Bulkachuwa na Jam’iyyar APC mai mulki, ya bayyana dalilansu na yunkurin tsige gwamnatin shugaba Muhammad Buhari.

    Daga cikin dalilan da ya bayyana a wata hira da yayi ta musamman da kamfanin labarai na BBC Hausa, yace, “Mun bi Dokar Kasa, wacce ta bamu dama mu bawa shugaban kasa damar samun cikakken ‘yan ci na shawo kan kalubalen tsaro, kuma mun ba shi kudade isassu.

    “Tsarin mulki ya bamu dama, in munyi iyaka yin mu, to mu zauna mu gaya wa shugaban kasa Gaskiya, cewa ya gaza.

    “Don haka, muka zauna muka tattauna, muka yanke shawarar mu ba wa shugaban kasa makonni 6 na tafiya hutun mu, akawo sauyi ga kalubalen tsaro kafin mu dawo, wanda Mun gode Allah mun fara ganin sauye-sauye a hedikwatar tsaro ta Jami’an soji.

    “Duk Sanatoci sun yarda sai ‘yan kalilan da tsige shugaba Buhari bisa dokar kasa in ba a samu sauyi ba a fannin tsaron Kasar nan har muka dawo.”

    A Wani Labari Kuma Buhari Ya Ja Kunnen Hafsoshin Tsaron Nijeriya Cewa “Asarar Rayukan Ya Isa Haka”

    Shugaban, a wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Garba Shehu, ya fitar a ranar Talata, bayan rahotannin da aka samu kan asarar rayuka da dama a hare-haren, ya kuma kara ba da tabbacin goyon bayan gwamnatin tarayya ga jihohi, inda ya kara da cewa “Mun ba Shugabannin tsaro cikakken ‘yanci don kawo karshen ‘yan Ta’adda da munanan ta’asarsu.”

    “Na yi Allah-wadai da wadannan munanan hare-haren a kasar nan. Ina so in tabbatar wa jihohi cewa duk wani goyon baya da ya dace, don kawo karshen Hare-haren ‘yan Ta’adda daga gwamnatin tarayya zamu tabbatar musu.

    “Damuwa ta a kullum tana tare da iyalan Wadanda suka rasa ‘yan uwansu da abokansu.

    “Allah ya sa wadanda suka ji rauni su warke cikin gaggawa,” in ji shugaba Buhari.

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Abduljalal on August 12, 2022 3:46 pm

      Allah wadaran gwamnatin buhari

      Reply
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.