AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Waiyazubillahi! Yadda Ya Kashe Mahaifinsa Saboda Ya Yiwa Mahaifiyarsa Kishiya
    News

    Waiyazubillahi! Yadda Ya Kashe Mahaifinsa Saboda Ya Yiwa Mahaifiyarsa Kishiya

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 5, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Labarin da muke samu shine lani matashi mai suna Kazeem Muhammad ya tsere bayan kashe mahaifinsa saboda yi wa mahaifiyarsa kishiya shekara daya da ta gabata a garin Suleja da ke jihar Neja.

    Wannan abu hakika ya daurewa mutane kai ganin yadda ya nuna kishi fiye da mahaifiyarta.

    Dan uwan marigayin mai suna Isah ya shaida wa yan jarida cewa bayan ya kwada wa mahifin nasa falanki a ka, take Kazeem ya cika wandonsa da iska.

    Ya ce, “Matashin na shaye-shaye sosai, don haka ya saba aikata abubuwan da ba su kamata ba.

    “Ranar Laraba da safe ne sa-in-sa ta shiga tsakaninsa da mahifin nasa, sai ya kwada masa wani falankin katako da ke gurin, kuma take ya fadi, shi kuma ganin haka sai ya tsere.

    “Mun kai shi asibiti domin ba shi agajin gaggawa, amma a nan take ya ce ga garinku nan,” inji dan uwan marigayin.

    Ya kuma ce tuni suka sanar da hukumomin da suka kamata domin daukar mataki, sannan suka binne gawar mamacin.

    Sai dai Rundunar ’Yan Sandan yankin ta ki cewa uffan a kan lamarin. Yayinda haryanzun ana jira aji ta bakinsu akan gaskiyar lamarin.

    Wadannan abubuwa ne da suka saba faruwa a kasar kasar Hausa, sai dai muna rokon Allah ya kawo mana karshen wannan masifu.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.