AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin
    News

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiNovember 27, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Wani dalibin ajin karshe a Jami’ar Tarayya ta Kashere da ke Jihar Gombe, Nalkur Zwalnan Lar ya kashe kansa saboda ya gaza mallakar wayar salula ta naira dubu hamsin.

    Wakilinmu ya ruwaito cewa, Nalkur ya kashe kansa ne a unguwar Santuraki da ke garin Kashere a daren ranar Laraba.

    Majiyar rahoton ta ce dalibin wanda ke karatu a Tsangayar Nazarin Koyarwa ya kashe kansa ne bayan ya sha guba, kuma bayan hakarsa ba ta cimma ruwa ba ya rataye kansa a jikin wata itaciya.

    Cikin wani sako da ya rubuta da hannunsa kafin wannan danyen aiki, dalibin ya yi wa yayyansa maza godiya wanda ya ce sun yi masa komai a rayuwa.

    Haka kuma, dalibin ya bukaci mahaifiyarsa wadda ya bayyana a matsayin mafificiyar uwa a duniya da ta dauki dangana.

    A cikin wasikar, dalibin ya bayyana cewa bai san dadin rayuwa ba, yana mai ikirarin cewa mahaifinsa ya mallaki miliyoyin naira amma shi kuwa ko wayar naira dubu hamsin ta gagare shi.

    Marigayin ya kuma zayyana sunayen mutanen da suke binsa bashi da kuma yadda za su samu kudinsu.

    Kazalika, ya nema gafarar wasu mutum biyu da ya bayyana sunayensu –Favour da Comfort.

    Da aka tuntubi Shugaban Sashen Tsare-Tsare da Bayanai na Jam’iar Kashere, Suleyman Malami Ahmed, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce za su fitar da jawabi a nan gaba da zarar sun kammala bincike.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022

    Matashi Yakai Iyayen Budurwarsa Kotu Saboda Zasu Aurar Da Ita A Kano

    November 22, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.