AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Yadda Aka Kama Malamin Jami’a Yana Kokarin Lalata Da Dalibarsa A Kano
    News

    Yadda Aka Kama Malamin Jami’a Yana Kokarin Lalata Da Dalibarsa A Kano

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiNovember 12, 2022Updated:November 12, 2022No Comments4 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    A ziyarar da tawagar Adikon Zamani ta kai Jamai’ar Bayero da ke Kano, wasu dalibai mata da maza sun shaida wa BBC yadda wasu baragurbi daga cikin malamansu suke nemansu domin yin lalata da su.

    Daya daga cikinsu ta ce “wani malaminmu ya taba cewa yana so na, amma ko da na nuna masa cewa ni ba wannan ne ya kawo ni makaranta ba sai ya yi min barazanar cewa idan dai ban ba shi hadin kai ba, to ni ma lokaci zai zo da zan fado hannunsa.

    “Ganin cewa mun yi haka a dole na fasa daukar madda (course) dinsa saboda tsoron kada na fada tarkonsa, kuma Allah ya taimake ni maddar tasa ba ta dole ba ce, don haka kawai sai na ki dauka,” a cewar dalibar wadda ta nemi a sakaya sunanta.

    A nata bangaren, Jami’ar Bayero ta ce tana da ka’idoji masu tsauri na tunkarar irin wadannan korafe-korafe.

    Shugaban sashin kula da jin dadin dalibai na jami’ar Dr Shamsudden Umar, ya shaida wa BBC cewa makarantar na daya daga cikin wuraren da ba a daurewa irin wannan dabi’a gindi, sannan ya nemi dalibai da kada su ji tsoro wurin bayyana duk wanda ya nemi cin zarafinsu.

    Haka shi ma wani dalibi namiji, ya shaida wa BBC yadda ya fada tarkon wani malami kawai saboda yana da alaka da wata daliba da malamin yake nema.

    “Lamarin sai da ya kai malamin da abokinsa suka kira ni har ofis suka titsiye ni kan alaka ta da ita saboda suna zargin ta gaya mana cewa yana nemanta bayan da wata kawarta ta kai mai tsegumi.”

    Sai da na je kare kaina, amma hakan bai yi wani tasiri ba,” a cewar dalibin wanda shi ma ya nemi a boye sunansa.

    Cin zarafi ta hanyar lalata laifi ne a Najeriya, amma duk da haka ana ci gaba da samun aukuwar lamura irin wannan a jami’o’in Najeriya.

    A kwanan nan ne wata dalibar Jami’ar Obafemi Awolowo ta tona asirin wani malamin Jami’ar da ya nemi yin lalata da ita.

    Dalibar mai suna Monica Osagie ta nadi tattaunawar da ta yi da wani malaminta da ya nemi yin lalata da ita domin ya ba ta damar cin jarabawa tare da watsa tattaunawar.

    Lamatrin ya ja hankalin jama’a a ciki da wajen Najeriya.

    A kwanan nan ne wata dalibar Jami’ar Obafemi Awolowo ta tona asirin wani malamin Jami’ar da ya nemi yin lalata da ita.

    Dalibar mai suna Monica Osagie ta nadi tattaunawar da ta yi da wani malaminta da ya nemi yin lalata da ita domin ya ba ta damar cin jarabawa tare da watsa tattaunawar.

    Lamatrin ya ja hankalin jama’a a ciki da wajen Najeriya.

    Dalibar ta Jami’ar Obafemi Awolowo, ta watsa tattaunawar tata ne da Farfesa Richard Akindele, wanda ke koyarwa a sashin harkokin kasuwanci da hada-hadar kudi na jami’ar, a shafukan sada zumunta.

    Lamarin dai ya kai ga jami’ar kafa kwamitin bincike wanda a karshe ya sami malamin da laifi kuma aka kore shi daga aiki.

    Mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Eyitope Ogunbodede, ya ce an kori Farfesa Richard Akindele ne bayan da ya amsa laifin kulla alaka da daya daga cikin dalibansa ta hanyar da ba ta dace ba.

    “Farfesa Akindele ya nemi yin lalata da Monica Osagie domin sauya maki kashi 33 da ta ci zuwa adadin da zai ba ta damar tsallakewa,” a cewar Ogunbodede.

    Kusan wannan ne karo na farko da za a iya cewa wata makaranta ta dauki hukunci a bainar jama’a kan irin wannan aika-aika da aka dade ana zargin wasu malaman jami’a da aikata wa.

    Kuma babu shakka matakin da Monica ta dauka na tona asirin malamin ya samu karbuwa a wurin daliban jami’a a sassan kasar da ma sauran jama’ar gari, saboda halayya ce da ta dade tana faruwa ba wai a Najeriya kawai ba.

    Sai dai a cewar Dr Shamsudden Umar ya ce BUK ta bude wani ofis na musamman mai cin gashin kansa domin bai wa dalibai damar kai korafe-korafe masu kama da irin wadannan.

    Ya kara da cewa babu wani malami da za a dagawa kafa idan aka same shi da laifi, yana mai bai wa dalibai kwarin gwiwa domin su bayyana duk wani bara-gurbin malami da suka sani.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.