Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    Yadda Aka Kama Mijin Daya Ajiye Budurwasa Wanda Yayi Karyar Kanwarsce A Dakin Matarsa Yana Lalata Da Ita

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiNovember 2, 2022No Comments2 Mins Read

    Alkalin wani kotu dake Oke-Ogbere a garin Ibadan, na jihar Oyo ya warware auren wata mata mai suna Temilade Oyeyemi da mijin ta Ayo Oyeyemi a ranar Alhamis.

    Alkalin kotun mai suna Sulaiman Olaniyi ya warware auren ma’auratan ne a dalilin gamsassun shaidu da aka bayyanar a gabansa wanda suka nuna cewa lallai Ayo makaryaci ne kuma maciyi amanar matarsa ne.

    Temilade mai shekaru 28 ta bayyana wa kotu yadda mijinta ya ci amanar ta bayan ya gabatar da budurwarsa a matsayin kanwar mahaifiyarsa wa ita da iyayenta.

    ” Wannan na daga cikin dalilan da yasa iyaye na suka amince mu yi aure shekara uku da suka wuce.

    Temilade ta ce ta fara fahimtar karya da cin amanar da Ayo yayi mata ne wata ranar da da dare bayan auren su inda ta gan shi kuru-kuru yana saduwa da matar da ya gabatar a matsayin kanwar mahaifiyar sa.

    ” Kafin wannan rana dama kullum idan dare ya yi sai ya tashi daga kan gadon da muke kwance tare ya koma kasa inda wannan mata ke kwance. Idan na yi magana sai yace ai ya kwanta a kasa ne sabo da zafi ya yi yawa.

    “Bayan na samu ciki sai ya juya min baya ya fara tozarta ni ya daina kula ni kwata-kwata.

    Shi kan sa Mahifin sa da ya bayyana a kotun dakan sa ya roki kotu da ta raba wannan aure, domin cin amanar ta yi yawa.

    ” Ayo ya bani kunya sannan ya tozartani a idunun duniya ace a a matsayin sa na da na. Dama can ya dai na kulawa da ni, hasali ma kawai ganin sa muka yi wai har yayi aure ya na ma da da.”

    Sai dai kuma Ayo ya karyata wannan zargi da ake masa. Ya ce duk zuki ta malle ne ba haka bane.

    Yace ” Tun da na auri Temilade ni ne wanki, ni ne shara kuma ni ne nake fita in nemo na kawo mata. Ba irin wannan magana.”

    A karshe alkalin kotun Sulaiman Olaniyi ya raba auren, sannan ya ce ita Temi ne zata ci gaba da rike dan nasu.

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.