AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Yadda Ya Kashe Makwabcinsa Saboda Gudun Biyan Bashi
    News

    Yadda Ya Kashe Makwabcinsa Saboda Gudun Biyan Bashi

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiAugust 10, 2022No Comments3 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Kamar yadda shafin amihad.com ya sabo kawo muku labarai masu daukar hankali da ban mamaki to a wannan karon ma mun kawo muku labarin yadda wani marar imani ya kashe makwancinsa kawai saboda gudun biyansa bashin da yake binsa.

    Mun samo wannan labarri daga shafin Aminiya inda labarin yake cewa:

    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo ta damke wani mutum kan zargin kashe makwabcinsa da ke bin sa bashi.

    Mai magana da yawun rundunar, Adewale Osifeso, ya ce wanda ake zargin ya yi ikirarin ya kashe makwabcin nasa ne don kubuta daga bashin da yake bin sa.

    Ya ce bayan kashe marigayin, wanda ake zargin ya dauki motar da ya bayar a matsayin jingina na bashin da ya karba ya tsere da ita.

    Da yake bayani sa’ilin da suke gabatar da wanda ake zargin ga manema labarai a ranar Talata, Osifeso ya ce wani mai suna Adesope Adeolu ne ya kai rahoto ofishin ’yan sanda da ke Eleyele bayan faruwar lamarin cewa ya ga kofar makwabcinsa a bude, wanda bai saba aukuwa ba.

    “Ko da ya bincika, sai ya tarar da makwabcinsa Olusegun Rufus, kwance cikin jini a mace, inda ya yi zargin mai yiwuwa kashe shi aka yi,” inji jami’in.

    Ya ce bayan bincike da bayanan sirri da aka tattara, aka kama wanda ake zargin wanda ya tabbatar shi ne ya kashe Rufus don ya kubuta daga bashin da yake bin sa.

    “Haka nan, an gano motar da ya jinginar don karbar bashin wadda ya yi amfani da ita ya tsere,” in ji shi.

     

    A Wani Labarin Kuma Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 3, Ta Rushe Gidaje 495 A Kano

    Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar Kano (SEMA), ta ce ambaliyar ruwa ta kashe mutane uku tare da raba iyalai 495 da muhallansu a Karamar Hukumar Ajingi da ke jihar.

    Babban Sakataren hukumar, dakta Saleh Jili ne, ya bayyana hakan a ranar Litinin a Ajingi, yayin da yake raba kayan agaji ga wadanda abin ya shafa, ciki har da iyalan mutane uku da suka rasu.

    Jili ya lissafa yankunan da lamarin ya shafa da su hada da Toranke, Kara Malama, Chuna da Balare.

    Ya ce lamarin da ya faru bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya a ranakun 3 da 4 ga watan Agusta, ya shafi mutane 495 da lamarin ya rutsa da su, ya kuma kashe uku da jikkata mutum daya.

    “A madadin Gwamna Abdullahi Ganduje, mun zo nan ne domin jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da raba musu wasu kayayyaki.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.