AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    Home » Yajin Aiki Yasa Wani Dalibin Jami’a Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa Sannan Ya Karya Kafar Mahaifinsa
    News

    Yajin Aiki Yasa Wani Dalibin Jami’a Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa Sannan Ya Karya Kafar Mahaifinsa

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiSeptember 3, 2022Updated:September 3, 2022No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Pinterest Email

    Majiyarmu ta shaida mana cewa tun a baya Najib ya sha shan alwashin cewar sai ya kashe matar mai suna Asiya Muhammad saboda yadda ya ce tana takura masa a gidan.

    Sai dai majiyar, wacce ta nemi a sakaya sunanta ba ta tabbatar da ko mahaifiyar shi Najib din tana gidan ko tana tare da mahaifin ba ko kuma a’a.

    Kazalika, an ce bayan ya biyo kanwar shi da tabaryar a guje zuwa kofar gida inda ya tsaya yana cewa duk wanda ya matso kusa da shi zai kashe shi.

    Amma a nan ne a cewar majiyar jama’ar unguwar suka yi tara-tara suka kama shi sannan suka mika wa ’yan sanda.
    Dalibin da ke aji uku a Jami’a mai suna Najeeb Umar Shehu, 24, ya yi ta dukan kishiyar mahaifiyarsa, Hajiya Hasiya Galadima, wacce tsohuwar ma’aikaciya ce a gwamnatin jihar Katsina da tabarya har rai ya yi halinsa.

    Da yake bayyana abin da ya faru, Mustapha Umar, ya tabbatar da cewa Najeeb ya dade yana barazanar kashe Hajiya Hasiya, saboda yana zargin ta da hannu wajen mutuwar auren Mahaifiyarsa, kuma an sha kai maganar wajen ‘yan sanda, amma ba a dauki wani mataki ba.

    Mustapha ya bayyana cewa kafin Najeeb ya je gidan nasu, sai da ya tatul da kwaya, inda ya shiga dakin girki ya dauko tabarya, ya je ya rutsa marigayiyar a daki ya shiga dukan ta, har sai da ya tabbatar rai ya yi halinsa.

    Lokacin da mahaifinsa, Alhaji Umar Shehu Balele, wanda ma’aikaci ne a Ma’aikatar Ilimin Jihar Katsina ya ji hayaniya, ya fito da nufin jin abin da yake faruwa, shi ma sai ya buga masa tabaryar ya karya shi a kafa, kuma ya fadi sumamme.

    Yayin da aka yi jana’izar marigayiyar kamar yadda addinin musulunci ya tanada, shi kuwa Malam Umar yana kwance a asibiti bangaren kula da kashi yake amsar magani.

    Jama’ar unguwa ne suka yi wa Najeeb tara-tara suka kama shi suka mika shi ga jami’an tsaro.

    Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Katsina, Gambo Isah ya tabbatar da faruwar lamarin, tare da bayyana cewa za su gurfanar da shi a gaban kotu da zarar sun kammala bincike.

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr WhatsApp Email

    Related Posts

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022

    Yadda Aka Kama Malamin Addini Yana Lalata Da Yan Mata Biyu Yan Uwan Juna

    November 23, 2022
    Add A Comment

    Leave A Reply Cancel Reply

    Check Also

    Ya Kamata Kusan Da Wadannan Tsaruka Na Tallafi Da Ake Bawa Yan Nigeria

    January 27, 2023

    FG Begins SMEDAN ₦1.5m Loan – Application Portal

    January 20, 2023

    How to Obtain an Ecowas ePassport as a Holder of a Nigerian Passport

    January 20, 2023

    Easy Way to Apply for a Visa in Nigeria

    January 20, 2023

    Apply 2023 Microfinance Bank Kaduna Recruitment

    January 20, 2023
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2023 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.