Close Menu
    AMIHAD.COM
    • Admission
    • Education
    • Finance
    • Scholarship
    • Tech
    • Visa
    AMIHAD.COM
    News

    Bikin Sallah Yasa Gwamna Ganduje Ya Yiwa Mutum 13 Da Aka Yankewa Hukuncin Kisa Afuwa

    Lucky MurakamiBy Lucky MurakamiJuly 9, 2022No Comments1 Min Read

    Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi wa fursunoni 90 afuwa ciki har da mutum 13 da aka yanke wa hukuncin kisa.

    Gwamnan ya aiwatar da hakan ne sakamakon bikin Babbar Sallah.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun gidan gyaran hali na Najeriya reshen Jihar Kano Musbahu Lawan K Nassarawa ya saka wa hannu, gwamnan ya biya wa mutum 77 diyyar kuɗin da ake binsu domin fita daga gidan gyaran halin haka kuma akwai mutum 13 da aka yanke wa hukuncin kisa a baya da halayansu aka gamsu da su wanda hakan ya sa gwamnan ya yi musu afuwa.

    Haka kuma akwai fursunoni uku da aka yanke wa hukuncin kisa da gwamnan ya yi musu afuwa aka mayar da hukuncinsu ɗaurin rai da rai.

    Gwamna Ganduje ya kuma bai wa fursunonin shanu da raguna da shinkafa domin su ji daɗin Babbar Sallah.

    Related Posts

    Tofah Bayan Ganin Bidiyon Tinubu Yana Motsa Jiki, Malmai Sun Fara Zazzago Martani

    January 11, 2024

    Yadda Wata Matar Aure Ta Kama Mijinta Yana Cin Amanarta Ba Kunya Ba Tsoron Allah

    December 25, 2022

    Karshen Duniya Yazo: Yadda Dalibi Ya Dirkawa Malamarsa Ciki

    December 12, 2022

    Wani Dalibi Ya Kashe Kansa Saboda Ya Kasa Mallakar Wayar Naira Dubu Hamsin

    November 27, 2022

    An Kama Likitan Bogi Daya Dirkawa Yan Mata Hudu Ciki

    November 26, 2022

    Yadda Mahaifiyar Budurwa Tasa Saurayi Ya Dirkawa ‘Yarta Ciki

    November 25, 2022
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Privacy Policy
    • Terms & Conditions
    Copyright © 2025 AMIHAD.COM | All Right Reserved.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.